Ta’aziyya: Buhari Ya Tafi Daular Larabawa

Rahotannin dake shigo mana daga birnin tarayya Abuja na bayyana cewar Shugaban ƙasa Muhammadu Buhari ya ziyarci ƙasar Haɗaɗɗiyar Daular Larabawa ta United Arab Emirates (UAE) a ranar Alhamis.

Buhari zai gana da sabon Shugaban Ƙasa Sheikh Mohamed bin Zayed Al Nahyan a birnin Abu Dhabi don yi masa ta’aziyyar tsohon Shugaban Ƙasa Sheikh Khalifa bin Zayed Al Nahyan, a cewar wata sanarwa daga Fadar Shugaban Kasa ta fitar.

Kazalika zai taya sabon shugaban murna da kuma “sabunta ƙawancen da ke tsakanin Najeriya da UAE na tsawon shekaru”.

Ministocin da za su yi wa Buhari rakiya sun haɗa da Ministan Sadarwa Isa Pantami, da Ƙaramin Ministan Harkokin Waje Zubairu Dada, da Ministan Sufurin Jirgin Sama Hadi Sirika, da Ministan Abuja Mohammed Bello.

Ana sa ran Buhari zai koma gida Najeriya ranar Asabar.

Labarai Makamanta

Leave a Reply