Rahotannin dake shigo mana daga birnin tarayya Abuja na bayyana cewa, tsohon gwamnan jihar Ekiti Ayodele Fayose ya soki lamirin jama’ar Arewa na yawan aure da haihuwar ‘ya’ya ba bisa ka’ida ba, a matsayin babban dalilin da ke haifar da matsala a mulkin Shugaba Tinubu. An ruwaito Fayose na wannan furuci ne a tattaunawarsa da gidan talabijin na Channels, inda ya koka da yadda ‘yan arewa ke mayar da hannun agogo baya wajen ciyar da Najeriya gaba. ” Na yi hira da wasu ?an Arewa a lokacin da na ziyarci…
Read MoreCategory: Babban Labari
Babban Labari
Babu Dalilin Zanga-Zanga, Mun Magance Da Yawa Daga Cikin Bukatun Masu Zanga-Zangar – Fadar Shugaban Kasa
Gwamnatin tarayya ta ce yanzu babu bukatar yin zanga-zanga domin tuni ta fara tinkarar bukatun ‘yan Najeriya da ke ci gaba da kokawa. Da yake yiwa manema labarai jawabi bayan kammala taron majalisar zartarwa ta tarayya a Yau Litinin Ministan yada labarai da wayar da kan jama’a na kasa, Mohammed Idris, ya bayyana cewa, “Ana magance da yawa daga cikin batutuwan da masu shirya zanga-zangar suke tadawa, gwamnati na kokarin ganin an samar da abinci. .” “An raba shinkafar zuwa cibiyoyi daban-daban a fadin kasar nan, ana kuma sayar da…
Read MoreGwamnatin Kaduna Ta Dauki Matakin Hana Gudanar Da Duk Wata Zanga-Zanga A Jihar
Rahotannin dake shigo mana daga Jihar Kaduna na bayyana cewa Gwamna Uba Sani ya fara ?aukar matakai da nufin hana zanga-zangar da ake shirin yi a watan Agusta mai zuwa. Sanata Uba Sani ya gana da shugabannin hukumomin tsaro da sarakunan gargajiya, da roki matasa gami da wayar da kan mutane kan illar zanga-zanga Ya ce masu shirya wannan zanga zanga suna da wata ?oyayyar manufa ta tayar da tarzoma da gurgunta kasuwancin ?an ?asa. Gwamnan ya ?auki wannan matakin ne yayin da matasa ke shirin gudanar da zanga-zanga a…
Read MoreZanga-Zanga: Za Mu Canza Take Zuwa Ga Kiran Tinubu Ya Sauka Muddin Aka Taba Mu – Jagororin Zanga-Zanga
Masu shirya zangazanga a Najeriya sun ce kashe mutanensu ko kamasu, ko kuma raunatasu a lokacin zanga-zangar, zainsa su bukaci shugaban Tinubu ya yi murabus,’ don haka suke gargadi ga hukumomin tsaro, suka ce ba za su ja da baya ba har sai Tinubu da dukkan ministocinsa sun sauka, muddin abubuwan da suka lissafo suka faru. Jaridar The Gazzetta ta rawaito masu shirya zanga-zangar da suke wa take da #EndBadGovt a fadin kasar nan da ke tafe sun gargadi hukumomin tsaro cewa za a samu sakamako idan aka kai wa…
Read MoreZanga-Zanga: Mun Gano An Gayyato Sojojin Haya Daga Ketare – Shugaban ‘Yan Sanda
Babban Sufeton ‘yan sandan Najeriya Kayode Egbetokun ya shawarci masu shirya zanga-zanga da su sake tunani gabanin fara zanga-zangar. A yayin wani taron manema labarai da ya gudana a Abuja babban birin ?asar a yau Juma’a, Egbetokun ya ce rahotannin sirri sun tabbatar musu sojojin hayar ?asashen ?etare na shirin shiga zanga-zangar. Sai dai shugaban ‘yan sandan bai yi wani ?arin bayani kan zargin shigowar sojojin hayar ?asashen ketare ba cikin zanga-zangar. “Muna bibiyar yadda lamura ke faruwa kan zanga-zangar da take mana barazana, yayin da wasu ?ungiyoyi ke neman…
Read MoreZanga-Zangar Tsadar Rayuwa: Tinubu Ya Gana Da Manyan Malaman Musulunci
Rahotannin dake shigo mana daga birnin tarayya Abuja na bayyana cewa Shugaban ?asa Bola Ahmed Tinubu ya zauna da manyan Maluman Addinin Musulunci domin duba halin tsadar rayuwa da ‘yan Najeriya ke ciki. Rahotanni sun bayyana cewar manyan Malaman ?arkashin jagorancin Shugaban ?ungiyar Izala na ?asa Sheikh Abdullahi Bala Lau, sun shaida wa shugaban irin yanayin da ake ciki a kasar, sannan sun isar masa da sa?on Al’ummar Nijeriya Yayin ganawar ta yammacin Alhamis, Shugaban ?asa Bola Tinubu ya ce masu ?aukar nauyin zanga-zanga mutane ne da suka ?ora masalaharsu…
Read MoreAREWA 24: Ya Zama Dole A Sanya Dokar Ta Baci A Bangaren Gidajen Yada Labarai – Masana
A tattaunawar da masanan suka yi ta cikin shirin gidan talabijin na Liberty mai suna “Democracy In Practice” a turance, sun bayyana ?aukar matakin hakan a matsayin abin da ya wajaba duba da irin halin da ?asa ta tsinci kanta a ciki. Masanan wa?anda suka ha?a da babban sakatare na hukumar gidajen ya?a labarai ta Najeriya (BON) Dr Yemi Bamgbose, sai kuma Dr Emman Shehu daga cibiyar horar da ‘yan Jarida ta ?asa (IIJ) da Malam Sa’idu Carpenter ?wararren dan jarida. Dr Yemi Bamgbose ya koka da irin halin da…
Read MoreTsadar Rayuwa: Tinubu Ya Gargadi Masu Hankoron Gudanar Da Zanga-Zanga
Shugaban ?asa Bola Tinubu ya bu?aci ‘yan ?asar da kada su yi zanga-zangar nuna ?acin rai da matsin rayuwa a wata mai zuwa, kamar yadda Ministan Ya?a Labarai Mohammed Idris ya bayyana. Da yake magana da manema labarai jim ka?an bayan ganawa da shugaban ?asar a yau Talata, ministan ya ce Tinubu ya bu?aci masu shirya zanga-zangar da su dakata tukunna. “Game da maganar zanga-zanga, shugaban ?asa ya ce babu bu?atar yin ta tukunna,” in ji shi. “Ya nemi su jingine batun, ya nemi su jira su ji martanin da…
Read MoreBabu Wata Makarkashiya Da Ake Yi Wa Matatar Man Dangote- Gwamnatin Tarayya
Gwamnatin Najeriya ta fara yun?urin sasanta rikicin sa?anin da aka samu tsakanin matatar mai ta Dangote da kuma hukumomin da ke kula da harkokin man a ?asar. ?aramin Ministan Man Fetur Heineken Lokpobiri ya ce ya jagoranci wani zama da Aliko Dangote shugaban kamfanin Dangote, da Mele Kyari shugaban kamfanin NNPCL, da Farouk Ahmed shugaban hukumar Nigerian Midstream and Downstream Petroleum Regulatory Authority (NMDPRA), da Gbenga Komolafe shugaban Nigerian Upstream Petroleum Regulatory Commission (NUPRC) a yammacin yau Litinin. “Ganawar wani yun?uri ne na gano maganin matsalolin da matatar ke fuskanta,”…
Read MoreZargin Daukar Nauyin Ta’addanci: Turji Na Da Ciwon Hauka – Bello Matawalle
Rahotannin dake shigo mana daga birnin tarayya Abuja na bayyana cewa Ministan kasa a ma’aikatar tsaron Najeriya Bello Matawalle ya yi watsi da zargin da fitaccen ‘dan ta’adda Bello Turji ya masa na kawar da kai wajen yaki da ta’addanci lokacin da yake rike da kujerar gwamnan Zamfara. Turji ya danganta karuwar ayyukan ‘yan bindiga a jihar da kuma makwabtanta da manufofin gwamnatin Matawalle, inda ya bayyana cewar mazauna Shinkafi da Zurmi da kuma Isa dake Sokoto na da masaniya a kai. A martanin da ya gabatar ta hannun Dayemi…
Read MoreZanga-Zangar Tsadar Rayuwa: Kutungwilar ‘Yan Adawa Ne Da Niyyar Kifar Da Gwamnatin Tinubu – Fadar Shugaban Kasa
Mataimaki na musamman ga shugaban kasa kan harkokin yada labarai da dabaru, Bayo Onanuga, ya zargi magoya bayan Peter Obi, dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar Labour Party (LP) a zaben 2023 da yunkurin kifar da gwamnatin shugaban kasa Bola Tinubu da fakewa da zanga-zangar nuna fushin ?an Najeriya ga matsin rayuwa da ake fama da. Onanuga ya yi wannan zargin ne a cikin wata sanarwa da ya sanya a kan shafinsa sa ta X ranar Asabar. Sai dai bai bayar da wata hujja da za ta tabbatar da zargin…
Read MoreZanga-Zangar Tsadar Rayuwa: Ba Alfanu Bane Za Mu Kaucewa Faruwar Haka – Fadar Shugaban Kasa
Rahotannin dake shigo mana daga birnin tarayya Abuja na bayyana cewa, Gwamnatin tarayya ?arkashin jagorancin shugaban kasa Bola Tinubu ta gargadi Matasa masu aniyar shiga zanga-zangar tsadar rayuwa da cewa su dakata domin ba alfanu bace ga ?asar. Ministan ya?a labarai Mohammed Idria ne ya bayyana hakan lokacin da yake tsokaci dangane da shirin da wasu gungun jama’a ke yi na shirya zanga-zanga a ?arshen wata, a wata zantawa da ya yi da gidan rediyon BBC Hausa. Mohammed Idria ya ?ara da cewa Gwamnatin tarayya ta yi kyakkyawan tanadi na…
Read MoreTsadar Rayuwa: Gamayyar Kungiyoyin Arewa Sun Ba Tinubu Wa’adin Mako Guda
Gamayyar ?ungiyoyin arewacin Najeriya ta CNG, ta bai wa shugaban ?asar Ahmed Bola Tinubu wa’adin mako guda da ya hanzarta tare da yin nazari game da halin da al’ummar ?asar ke ciki, tare da ?aukar matakan gaggawa da za su kawo wa ?an Najeriyar sau?in rayuwa. ?ungiyar dai ta ce dole ce ta sa daukar wannan mataki sakamakon yadda ake ci gaba da fuskantar matsin rayuwa musaman tashin farashin kayayyaki a ?aukacin fa?in ?asar. Gamayar ?ungiyoyin arewacin ta Najeriya ta ce, lamarin ?angin da ake fama da shi a ?asar…
Read MoreTsadar Rayuwa: ‘Yan Majalisar Wakilai Sun Sadaukar Da Rabin Albashinsu Na Wata Shidda
Rahotannin dake shigo mana daga birnin tarayya Abuja na bayyana cewa ?an majalisar wakilan Najeriya sun amince da a zabtare kaso 50 na albashinsu na tsawon watanni shida a wani mataki na nuna tausayawa ga yanayin matsin tattalin arzi?i da yunwa da ?an Najeriya ke ciki a halin yanzu. Wannan dai ya biyo bayan amincewa da gyaran ga bu?atar da mataimakin shugaban majalisa, Benjamin Kalu ya yi na bu?atar ?an majalisar da su sadaukar da kaso 50 na albashin nasu na naira 600,000 da suke kar?a. Hon Benjamin Kalu ya…
Read MoreTinubu Ya Bukaci Majalisa Ta Amince Da Karin Tiriliyan 6.2 A Kasafin Kudin 2024
Shugaban ?asa Bola Tinubu, ya bukaci majalisar dattawa da ta yi wa dokar kasafi ta 2024 da kuma dokar kudi ta 2023 gyaran fuska ta hanyar amincewa da ?arin naira tiriliyan 6.2 a cikin kasafin ku?in. Bu?atar ta Tinubu na ?unshe ne a cikin wata wasi?a da ya aika wa shugaban majalisar dattawa, Godswill Akpabio, kuma aka karanta a zauren majalisa ranar Laraba. A cikin wasikar, Shugaban ya ce yana son ?aukar matakin ne bisa dogaro da sashe na 58, ?aramin sashe na biyu na kundin tsarin mulkin Najeriya na…
Read MoreGwamnatin Tarayya Ta Roki Gwamnoni Su Tabbatar Shinkafar Da Aka Basu Ta Kai Ga Talakawa
Rahotannin dake shigo mana daga birnin tarayya Abuja na bayyana cewa Gwamnatin tarayya karkashin jagorancin shugaban kasa Bola Tinubu ta yi kira ga gwamnonin Jihohi su tabbatar shinkafar da aka basu takai ga hannun talakawa. Mnistan ya?a labarai Alhaji Mohammed Idris ne ya yi wannan kiran a Abuja, lokacin da yake karin haske dangane da matakan da gwamnatin Tinubu ke ?auka na magance matsalar yunwa dake addabar ‘yan ?asar. A ranar Litinin ?in wannan mako ne gwamnatin tarayya ta sanar cewa ta bai wa gwamnoni tirelolin shinkafa wa?anda za su…
Read MoreBabu Gaskiya A Zargin Sanata Ndume Na Cewar Ba A Ganin Tinubu – APC
Jam’iyyar APC ta yi abin da Bahaushe ke cewa ‘ka fi mai kora sosawa’, yayin da ta nuna jin ciwon zafafan kalaman da Sanata Ali Ndume ya yi wa Shugaban ?asa Bola Tinubu. APC ta yi masa raddin cewa kasa samun damar ganawar da Ndume ya yi da Tinubu ba zai ta?a zama dalili ko hujjar cewa wasu sun kange shugaban ?asar daga ganawa da ‘yan Najeriya ba. Sakataren Ya?a Labarai na APC na ?asa, Felix Morka ne ya yi wa Ndume wannan raddi, wanda ke ?unshe cikin sanarwar da…
Read MoreTinubu Zai Binciki Diddigin Kwangilolin Tituna Da Gwamnatin Buhari Ta Bayar
Shugaban ?asa Bola Tinubu ya bada umarnin a binciki dukkan kwangilolin kwantai ?in ginin titina da ya gada, musamman wa?anda aka ce su na bu?atar ?arin ku?i a Ma’aikatar Ayyuka, domin tantance gaskiya, bin-diddigi da kuma ?a’ida wajen ?arasa ayyukan. Ministan Ya?a Labarai da Wayar da Kai, Mohammed Idris ne ya bayyana haka, lokacin da yake wa manema labarai ?arin bayani a Fadar Shugaban ?asa, bayan tashi daga Taron Majalisar Zartaswa a ranar Laraba. Ya ce majalisar zartarwa ta yanke shawarar jingine ayyukan kwangilolin Ma’aikatar Ayyuka ta Tarayya, wa?anda gwamnatin…
Read MoreMuna Maraba Da Hukuncin Kotu Kan ‘Yancin Kananan Hukumomi – Gwamnoni
Kungiyar gwamnonin Najeriya ta ce ta yi maraba da hukuncin kotun ?olin ?asar wadda ta umarci gwamnonin su daina ri?e wa ?ananan hukumomi ku?a?ensu da ake ware musu daga asusun gwamnatin tarayya. Shugaban ?ungiyar, wanda kuma shi ne gwamnan jihar Kwara, AbdulRazaq AbdulRahman ya ce ?ungiyarsu za ta yi biyayya ga hukuncin kotun, yana mai cewa a yanzu lauyoyinsu sun bu?aci kwafin hukuncin kotun wanda za yi nazari a kai. Ya ?ara da cewa gwamnonin na murna da karkasa iko dangane da ‘yancin ?ananan hukumomin. ”Hakan zai rage wa gwamnoni…
Read MoreGwamnoni Sai Hakuri, Kotun Koli Ta Tabbatar Da Cin Gashin Kan Kananan Hukumomi
Kotun koli ta tabbatar da cin gashin kan kananan hukumomi 774 na Najeriya, ku?a?en su su shiga aljihun su darek ba tare da gwamnoni sun yi musu katsalandan ba. A hukuncin da ta yanke a ranar Alhamis, kwamitin mutane bakwai na kotun ya amince da kararrakin da gwamnatin tarayya ta gabatar na karfafa ‘yancin kananan hukumomin kasar nan. ?aya daga cikin mambobin kwamitin, Emmanuel Agim, wanda ya gabatar da hukuncin kotun, ya ce daga ranar Alhamis ya kamata kananan hukumomin kasar nan su karbi kason su kai tsaye daga hannun…
Read More