Ketare: An Kashe Shugaban Hamas Isma’il Haniyeh A Tehran

IMG 20240731 WA0033

Kungiyar Hamas ta ce an kashe shugaban ta Ismail Haniyeh a birnin Tehran na Iran. Wata sanarwa da ?ungiyar ta fitar yau da safe ta ce an kashe Haniyeh ne a gidansa da ke Tehran, a ziyarar da yake domin halartar bikin rantsar da sabon shugaban Iran, Masoud Pezeshkian. ?ungiyar falas?inawan mai ri?e da iko a Gaza ta ce Isra’ila ce ta kashe shugaban nata, Ismail Haniyeh, yayin da yake halartar rantsar da sabon shugaban Iran. ?ungiyar Hamas ta bayyana kisan a matsayin babban laifi wanda martanin sa ba zai…

Read More

Ana Tafka Kazamar Sata Kowace Rana A Najeriya – ‘Yan Sandan Kasa Da Kasa

IMG 20240226 WA0252

Hukumar ‘yan sanda ta ?asa da ?asa (Interpol) ta bayyana cewa ana wawure dubban daruruwan daloli daga Najeriya Zuwa Wasu kasashen Duniya a kowacce sa’a. Wannan bayanin ya fito ne a Abuja ranar Litinin ta hannun mataimakin shugaban hukumar ‘yan sanda ta Interpol mai kula da Afrika, Garba Umar, yayin bu?e taron horar da jami’an tsaro na Najeriya na kwanaki hudu a makarantar horas da masu yi wa tattalin arzikin kasa zagon kasa ta EFCC. A cewar Garba Umar, safarar kudaden haram ta kai wani mataki mai ban tsoro a…

Read More

Makon ‘Yan Jarida: Gwamnatin Kaduna Ta Sha Alwashin Hada Hannu Da Kungiyar ‘Yan Jarida

IMG 20240731 075644

Rahotannin dake shigo mana daga Jihar Kaduna, na bayyana cewa Gwamna Malam Uba Sani ya bayyana cewa zai hada kai da kungiyar ‘yan Jarida ta Najeriya (NUJ), reshen Jihar Kaduna domin ganin Jihar ta samu ci gaba ta fuskar tattalin arziki, zamantakewa da siyasa a karkashin Gwamnatinsa. Gwamna Sani ya bayyana cewa ba za a yi watsi da rawar da ‘yan Jarida ke takawa wajen tallafawa Gwamnati ba, yana mai cewa gwamnatinsa ta ba da fifiko ga rikon amana da gaskiya a harkokin mulki. Gwamnan ya yi wannan jawabi ne…

Read More

Zanga-Zanga Na Iya Haifar Da Yunwa Da Ba A Taba Gani Ba A Najeriya – Kungiyar Kare Musulmi

Kungiyar Kare Muradun Musulman Najeriya (MURIC), ta garga?i masu shirya zanga-zanga cewa zanga-zangar fushin fama da yunwar da suke shirin tsunduma za ta iya haifar da gagarimar yunwar da ba a ta?a fuskanta ba. ?ungiyar ta ja hankalin matasa cewa su bi a hankali, su yi ha?uri, sannan kuma su amince a zauna teburin sulhu. Wannan matsayi da MURIC ta ?auka ta fitar da shi ne a ranar Talata, daga bakin Babban Daraktan Ishaq Akintola. “Matasan Najeriya wa?anda manyan ‘yan adawa ke ?aukar nauyi sun shirya fita zanga-zangar nuna fushin…

Read More

Yawan Haihuwa Da Auren Mata Rututu Na ‘Yan Arewa Ne, Ke Haifar Da Matsala A Mulkin Tinubu – Fayose

FB IMG 1722402837249

Rahotannin dake shigo mana daga birnin tarayya Abuja na bayyana cewa, tsohon gwamnan jihar Ekiti Ayodele Fayose ya soki lamirin jama’ar Arewa na yawan aure da haihuwar ‘ya’ya ba bisa ka’ida ba, a matsayin babban dalilin da ke haifar da matsala a mulkin Shugaba Tinubu. An ruwaito Fayose na wannan furuci ne a tattaunawarsa da gidan talabijin na Channels, inda ya koka da yadda ‘yan arewa ke mayar da hannun agogo baya wajen ciyar da Najeriya gaba. ” Na yi hira da wasu ?an Arewa a lokacin da na ziyarci…

Read More

Daga Waje Ne Aka Dauki Nauyin Shirya Zanga-Zangar Najeriya – Kashim Shettima

Kashim Shettima office portrait

Yayin da ake fama da tabarbarewar tattalin arziki da ke kara fusata jama’a kan Gwamnatin shugaba Bola Tinubu, mataimakin shugaban kasar Kashim Shettima ya zargi ‘yan Najeriya mazauna kasashen waje da cewa su ne ke da hannu wajen shirya zanga-zangar da za a yi a watan Agusta a fadin kasar, inda ya kira su ‘yan iska. Da yake jawabi a wajen wani daurin aure a Maiduguri, jihar Borno a ranar Asabar, Mista Shettima ya bayyana wadanda suka shirya zanga-zangar na watan Agusta a matsayin ‘yan fashi da wawaye a ?asashen…

Read More

Kotun Koli Ta Sanar Da Ranar Ritayar Alkalin Alkalai

IMG 20240730 WA0189

Kotun koli ta sanar da cewa Olukayode Ariwoola zai yi ritaya a matsayin Alkalin Alkalan Najeriya a ranar 22 ga watan Agusta. A wata sanarwa da aka fitar a ranar Litinin, Festus Akande mai magana da yawun kotun koli ya ce za a gudanar da zaman kotun na ban kwana domin girmamawa ga alkalin alkalan wanda ke cika shekaru 70 na ritaya. Akande ya kuma ce kotun kolin ta fara hutun ta na shekara a ranar 22 ga watan Yuli inda za ta dawo a ranar 23 ga watan Satumba…

Read More

Zanga-Zanga: Ba Za Mu Amince A Kifar Da Gwamnatin Tinubu Ba – Shugabannin APC

images 2024 03 06T195109.222

Shugabannin jam’iyyar APC na jihohi 36 da Abuja sun ci alwashin cewa ba za su zuba ido su na kallo wasu batagari su kifar da gwamnatin shugaba Bola Ahmed Tinubu ba da sunan zanga-zanga. Sakataren kungiyar ciyamonin APC na ?asa, wanda kuma shine Ciyaman din jam’iyyar a Cross River, Alphonsus Ogar Eba a taron manema labarai a shelkwatar jam’iyyar ta ?asa a yau Litinin ya ce zanga-zangar ta kwanaki goma wani shiri ne na kifar da gwamnatin Tinubu. Ciyamonin jam’iyyar sun yi garga?in cewa duk wanda ya gaje da zanga-zangar…

Read More

Babu Dalilin Zanga-Zanga, Mun Magance Da Yawa Daga Cikin Bukatun Masu Zanga-Zangar – Fadar Shugaban Kasa

IMG 20240225 WA0030

Gwamnatin tarayya ta ce yanzu babu bukatar yin zanga-zanga domin tuni ta fara tinkarar bukatun ‘yan Najeriya da ke ci gaba da kokawa. Da yake yiwa manema labarai jawabi bayan kammala taron majalisar zartarwa ta tarayya a Yau Litinin Ministan yada labarai da wayar da kan jama’a na kasa, Mohammed Idris, ya bayyana cewa, “Ana magance da yawa daga cikin batutuwan da masu shirya zanga-zangar suke tadawa, gwamnati na kokarin ganin an samar da abinci. .” “An raba shinkafar zuwa cibiyoyi daban-daban a fadin kasar nan, ana kuma sayar da…

Read More

Tsadar Rayuwa: A Akwatunan Zabe Ya Kamata Ku Nuna Fushi Ba A Zanga-Zanga Ba – Kwankwaso Ga Matasa

IMG 20240506 WA0135(1)

Madugun Jam’iyyar New Nigeria Peoples Party (NNPP) na kasa, Sanata Rabi’u Musa Kwankwaso, ya bukaci ‘yan Najeriya da su nemi sauyi ta hanyar dimokradiyya maimakon zanga-zanga. Kwankwaso Ya bayyana hakan ne A cikin wata sanarwa da shi da kan sa ya sanya wa hannu a ranar Jumma’a 26 ga Yuli, 2024 Ya shiga cikin rashin jin dadi da kan kiraye-kirayen zanga-zangar da matasan ke Shirin gudanarwa a duk fa’din Kasar. Sanata Kwankwaso ya jaddada cewa za a iya samun sauyi mai inganci kuma mai dorewa Amma t hanyar karfin zabe.

Read More

Jam’iyyun NNPP, APC Da PDP Sun Kaurace Wa Shiga Zanga-Zanga A Kano

IMG 20240229 WA0298

Rahotannin dake shigo mana daga Jihar Kano na bayyana cewa jam’iyyar NNPP mai mulki da na adawa da suka ha?a da APC da PDP a unguwar Dakata, ?aramar Hukumar Nassarawa a jihar Kano sun ha?a kai wajen kauracewa zanga-zangar da ake shirin yi kan matsin rayuwa a fadin kasar nan. Jam’iyyun, ta bakin ciyamonin su na ?aramar hukumar, sun yi kira ga al’umma da su kauracewa shiga zanga-zangar. A wani taron gangami da aka yi a Dakata Gidan Dagaci a jiya Asabar, Sabo Sambo (NNPP) da Umar Usman Usman (APC)…

Read More

‘Yan Bindiga Sun Sace Mai Martaba Sarkin Gobir A Sakkwato

FB IMG 1722229110981

Matsalar rashin tsaro na ci gaba da hana mutane bacci da idanu biyu rufe a wasu sassan Najeriya duk da kokarin da mahukunta ke yi na samun saukin matsalar. Wani abu da ke kara tabbatar da haka shi ne yadda ‘yan bindiga a ranar Asabar su ka sace basaraken daular Gobir da ke Sokoto, Sarkin Gobir na Gatawa Isah Muhammad Bawa. Yanzu haka ‘yan uwa da sauran jama’ar gari na ci gaba da nuna alhini a kan wannan lamari da ya faru da Sarkin Gobir wanda ba da jimawa ba…

Read More

Ba Domin Zuwan Tinubu Ba Da Najeriya Ta Wargaje – Ministan Ayyuka

Ministan ayyuka, David Umahi, ya bayyana cewa da Najeriya ta wargaje, idan ba don Allah ya kawo shugaba Bola Tinubu karagar mulki a wannan lokaci mai muhimmanci ba. Ya bayyana hakan ne yayin da ya bukaci matasa da su soke zanga-zangar da suke shirin yi da kuma tallafawa Gwamanti wajen bun?asa ababen more rayuwa. Da yake jawabi a wajen kaddamar da shirin Gwamnatin Tarayya mai taken “Operation Free Roads” a Abuja a karshen mako, Umahi ya bayyana kwarin gwiwar cewa shugaban kasar zai kawo sauyi a kasar idan aka kara…

Read More

Gwamnatin Kaduna Ta Dauki Matakin Hana Gudanar Da Duk Wata Zanga-Zanga A Jihar

IMG 20240310 WA0186

Rahotannin dake shigo mana daga Jihar Kaduna na bayyana cewa Gwamna Uba Sani ya fara ?aukar matakai da nufin hana zanga-zangar da ake shirin yi a watan Agusta mai zuwa. Sanata Uba Sani ya gana da shugabannin hukumomin tsaro da sarakunan gargajiya, da roki matasa gami da wayar da kan mutane kan illar zanga-zanga Ya ce masu shirya wannan zanga zanga suna da wata ?oyayyar manufa ta tayar da tarzoma da gurgunta kasuwancin ?an ?asa. Gwamnan ya ?auki wannan matakin ne yayin da matasa ke shirin gudanar da zanga-zanga a…

Read More

Zanga-Zanga: Za Mu Canza Take Zuwa Ga Kiran Tinubu Ya Sauka Muddin Aka Taba Mu – Jagororin Zanga-Zanga

IMG 20240226 WA0252

Masu shirya zangazanga a Najeriya sun ce kashe mutanensu ko kamasu, ko kuma raunatasu a lokacin zanga-zangar, zainsa su bukaci shugaban Tinubu ya yi murabus,’ don haka suke gargadi ga hukumomin tsaro, suka ce ba za su ja da baya ba har sai Tinubu da dukkan ministocinsa sun sauka, muddin abubuwan da suka lissafo suka faru. Jaridar The Gazzetta ta rawaito masu shirya zanga-zangar da suke wa take da #EndBadGovt a fadin kasar nan da ke tafe sun gargadi hukumomin tsaro cewa za a samu sakamako idan aka kai wa…

Read More

Yunkurin Hana Zanga-Zanga: Ba Zai Yiwu Ka Bugi Mutum Ka Hanashi Kuka Ba – Gargadin Afenifere Ga Tinubu

IMG 20240727 WA0024

Kungiyar Kare Muradin Yarabawa Zalla ta Afenifere, ?angaren shugabancin Ayo Adebanjo, ta bayyana cewa ta na goyon bayan fita a yi zanga-zanga kwanaki 10 da ake shirin farawa daga ranar 1 ga Agusta zuwa 10 ga Agusta. Kakakin Ya?a Labaran Afenifere ?angaren Ayo Adebanjo, Falmata Daniel ne ya bayyana cewa za a fita zanga-zanga saboda yadda Shugaba Bola Tinubu ya ?ora tattalin arzikin Najeriya a kan hanyar da ba ta ?ullewa, sai dai ta jefa ?asar nan cikin masifar ra?a?in tsadar rayuwa. Sakataren Ya?a Labarai na Afenifere, Justice Faloye ne…

Read More

Tattalin Arzikin Najeriya Na Kara Bunkasa – Fadar Shugaban Kasa

IMG 20240429 WA0024(1)

Shugaba Bola Tinubu ya tabbatar wa ‘yan kasar cewa tattalin arzikin kasar na kan hanyar farfadowa sannu a hankali amma kuma gwamnatinsa za ta kara yin kokarin biyan bukatunsu. A wata ganawa da ya yi da sarakunan gargajiya karkashin jagorancin mai alfarma Sarkin Musulmi, Muhammad Sa’ad Abubakar III, da Ooni na Ife, Oba Adeyeye Enitan Ogunwusi, a fadar gwamnati a yau Alhamis, shugaban ya bayyana matukar damuwarsa da halin da ‘yan kasa ke ciki da yayi alkawarin kara kulawa da bukatunsu. “Na himmatu ga wannan aikin kuma ba zan taba…

Read More

Tsadar Rayuwa: Zanga-Zanga ‘Yancin ‘Yan Najeriya Ne – Kungiyar Farfado Da Arewa

IMG 20240226 WA0252

Kungiyar Fafutikar Sake Farfa?o da Arewa ta bayyana goyon bayanta ga shirin zanga-zangar yaki da tsadar rayuwa a Najeriya. Kungiyar Fafutikar Sake Farfa?o da Arewa ta bayyana goyon bayanta ga shirin zanga-zangar yaki da tsadar rayuwa a Najeriya. Kungiyar ta ce tana da yakinin cewa matakin wannan zanga-zanga da ke tafe zai kawo sauyin da ake matukar bu?ata a kasar. Sakataren kungiyar, Dokta Salisu Nani Zigau, ya bayyana cewa dokar kasa ta ba ’yan Najeriya ’yancin yin zanga-zanga, kuma babbar dama ce gare su ta bayyana bukatunsu da neman adalci…

Read More

Tsadar Rayuwa: Wahalar Da Ake Sha Bata Kai Yadda Ake Surutu Ba – APC

images 2024 03 06T195109.222

Rahotannin dake shigo mana daga birnin tarayya Abuja na bayyana cewa Sakataren APC na ?asa, Surajudeen Basiru, ya bayyana cewa jadawalin ?ididdigar malejin tsadar rayuwa da tsadar kayan abinci a Najeriya, wanda Hukumar NBS ta fitar kwanan nan, akwai ?arin gishiri da zuzuta al?aluma a cikin bayanan. Basiru ya yi wannan furuci ne a ranar Laraba, lokacin da ake tattauna da shi a Gidan Talabijin na Channels. Basiru wanda lauya ne kuma tsohon Sanata, ya yi wannan bayanin daidai lokacin da gwamnatin tarayya ke ta ?o?arin kwantar wa matara hankali…

Read More

Zanga-Zanga: Mun Gano An Gayyato Sojojin Haya Daga Ketare – Shugaban ‘Yan Sanda

IMG 20240227 WA0004(1)

Babban Sufeton ‘yan sandan Najeriya Kayode Egbetokun ya shawarci masu shirya zanga-zanga da su sake tunani gabanin fara zanga-zangar. A yayin wani taron manema labarai da ya gudana a Abuja babban birin ?asar a yau Juma’a, Egbetokun ya ce rahotannin sirri sun tabbatar musu sojojin hayar ?asashen ?etare na shirin shiga zanga-zangar. Sai dai shugaban ‘yan sandan bai yi wani ?arin bayani kan zargin shigowar sojojin hayar ?asashen ketare ba cikin zanga-zangar. “Muna bibiyar yadda lamura ke faruwa kan zanga-zangar da take mana barazana, yayin da wasu ?ungiyoyi ke neman…

Read More