Shugaban kasa Muhammadu Buhari ya gana da wasu daga cikin fasinjojin jirgin kasan da ‘yan bindiga suka sace daga Abuja zuwa Kaduna a watan Maris.
Shugaban kasar ya gana da mutanen ne ranar Alhamis a fadar Aso Villa da ke Abuja kwana daya bayan sako karin mutum biyar da aka sace a jirgin kasan.
Ganawar tasu na zuwa ne makwanni kadan bayan ‘yan bindigar sun sha alwashin sace shi kansa shugaban kasar da kuma gwamnan Jihar Kaduna Nasir Elrufai.