Shugaban rukunin kamfanonin Dangote, Aliko Dangote ya gargadi yan Najeriya cewa kowa yayi tanadi kuma a kwana da shirin tsindumawa cikin karancin abinci da tsananin yunwa nan da watanni biyu masu zuwa.
Dangote ya ce dole gwamnati da masu ruwa da tsaki a harkar kasuwanci, masana;antu da noma su zauna a tattauna yadda za akawo karshen wannan matsala .
Ya kara da cewa tun yanzu an fara samun hauhawan farashin abubuwa kamar Taki, Masara, Alkama da dai sauran su.
” Za a samu karancin Masara da alkama a duniya saboda yakin da ake yi tsakanin Rasha da Ukraine. Wadannan kasashe sune ke samar da kashi 30 cikin 100 na uria da ake yin takin zamani da shi.