Gawurtaccen Dan Luwadi Zai Zama Alkali A Indiya

Rahotanni daga birnin New Delhi na kasar Indiya na bayyana cewar wani babban kwamitin Kotun ƙoli a kasar ya bayar da shawarar naɗa wanda ya fito ya bayyana cewa shi ɗan luwaɗi ne a matsayin alƙali, a wani abin da aka bayyana a matsayin “ci gaba” ga ƴancin masu neman jinsi ɗaya, kamar yadda ƴar jarida mai bayar da rahoto kan harakokin shari’a Suchitra Mohanty ta ruwaito.

Kwamitin da babban mai shari’a na ƙasar ke jagoranta ya bayar da sunan Saurabh Kirpal domin zama alƙalin Babbar Kotun Delhi.

Shawarar babban kwamitin shari’a na daga cikin matakan naɗa Alƙali a India kafin daga baya matakin ya samu amincewar gwamnati.

An yi imanin cewa gwamnatin Firaminista Narendra Modi za ta amince da naɗin Mista Kirpal a makwanni masu zuwa.

A 2018, Kotun ƙolin ƙasar ta ɗage haramcin luwaɗi da Maɗigo a wani hukuncin da aka bayyana babbar nasara ga masu neman jinsi ɗaya. Kuma Mista Kirpal shi ne lauyan da ya kare shari’ar da aka shigar.

Labarai Makamanta

Leave a Reply