Tsohon mataimakin shugaban ?asa, kuma ?an takarar Shugabancin ?asa a jam’iyyar PDP Atiku Abubakar ya jajantawa iyalan ?alibai mata da aka sace a kwalejin zamanantar da gandun daji dake Afaka, unguwar Mando ta jihar Kaduna.
“Satar ?aliban a Kaduna yazo bayan sati biyu da ku?utar da ?alibai mata 300 da aka sace a makarantar sakandiren mata ta gwamnati dake garin Jange?e dake jihar Zamfara wanda wasu ‘yan bindiga suka yi gaba dasu daga makarantarsu”.
“A shekarar 2014, Najeriya ta samu irin wannan matsalar, inda ‘yan ta’addan Boko Haram suka sace ?alibai mata sama da 200 a garin Chibok, dake jihar Borno. Har wane tsawon lokaci zamu ?auka a cikin wannan yanayin?” Inji Atiku.
“Haka zalika a shekarar 2018, Boko Haram ta sake yin awon gaba da ?alibai mata 110 a makarantar gwamnati dake Dapchi, jihar Yobe”.
Da yake magana akan lamarin a shafinsa na kafar sada zumuntar twitter, Atiku yace: “Abun damuwa ne matu?a a wannan yanayi da muke ciki, wanda kullum ake harin sace ?alibai mata a yankin Arewa.”
“Addu’a ta na tare da iyalan wa?anda abun ya shafa, kuma ina fatan babu wasu ku?a?e da za’a biya don ceto wa?annan yara.” Inji tsohon mataimakin shugaban ?asan.
Atiku Abubakar ya ?ara da cewa: “Babban abin tambayan anan shine; har wane lokaci zamu ?auka a cikin wannan yanayin?”