Rahotanni daga birnin tarayya Abuja na bayyana cewar Gwamnonin jam’iyyar APC mai mulki sun bayyana goyon bayansu ga Sanata Kashim Shettima a matsayin ɗan takarar mataimakin shugaban ƙasa a jam’iyyar a zaɓen 2023.
Gwamnonin sun bayyana goyon bayansu ne bayan sun gana da Buhari a Daura.
A ranar Lahadi ne ɗan takarar shugaban ƙasa Bola Tinubu ya sanar da tsohon gwamnan Borno Sanata Kashim Shettima a matsayin wanda zai masa takarar mataimaki.
Shugaban gwamnonin na APC Gwamnan jihar Kebbi Abubakar Atiku Bagudu da gwamnan Imo Hope Uzodimma waɗanda suka yi magana a madadin sauran gwamnonin sun ce da yawun bakinsu aka amince da Kashim a matsayin ɗan takarar mataimakin shugaban ƙasa.
Sun kuma yi alƙawalin yin aiki domin tabbatar da jam’iyyarsu ta APC ta yi nasara a zaɓen 2023.