Zamu Zamanantar Da Makarantun Allo -Hukumar Kula Da Harshen Larabci

YUNKURIN ZAMANTAR DA MAKARANTUN ALLOukumar dake kula da harshen larabci ta kasa (NBAIS) tayi alkawarin bada takardan shahada wato (Certificate) ga al’majirai tsangaya.

Hukumar za ta fara tantance dukkan daliban Tsangaya, Kolawa, Kotsawa, Gardawa da Alarammomi don basu takardan shaida wato (certificate) a fadin kasar nan don ganin ta inganta har kar ilimin Tsangaya.

Jihar Gombe na cikin sahun farko da zasu amma fana da shirin, wanda hukumar zata ai watar da zaran samu saukin wanna annoba da ya addabi duni wato covid19.

Yayin da suke baiyana dalilin su na zaban jihar Gombe a sahun farko na aiwatar da shirin, sun bayyana cewa, masu rike da madafu a jihar sun mai da hankali matuka a harkan ilimin Tsangaya, ganin haka yasa suka zabi jihar don ta zama na farko da zasu fara ai watar da shirin.

Labarai Makamanta

Leave a Reply