Zamfara: Matawalle Na Shirin Komawa APC

Rahotanni daga Gusau babban birnin Jihar Zamfara na bayyana cewa mai girma gwamna Bello Matawallen Maradun na shirye shiryen komawa jam’iyya mai mulki ta APC nan bada jimawa ba.

Tun a watannin baya ne aka ri?a ya?a jita-jita game da sauya shekar Gwamna Matawalle, wanda ya zama gwamnan jihar a karkashin jam’iyyar PDP, bayan hukuncin da Kotun Koli ta yanke kan rikicin da ya biyo bayan zaben fidda gwani na APC a Zamfara.

Tsohon gwamnan jihar Zamfara, Sanata Ahmed Sani Yarima, a shekarar da ta gabata ya bayyana cewa shirye-shirye na gudana kan komawar Matawalle APC.

A cewar wata majiya, rikicin da ya dabaibaye APC a jihar na daya daga cikin abubuwan da suka kawo tsaiko ga ficewar gwamnan daga jam’iyyar PDP.

An ruwaito cewa ana iya kulla yarjejeniyar a ranar Talata, 6 ga Afrilu lokacin da tawagar gwamnatin tarayya za ta ziyarci Zamfara don yi wa gwamnan jaje kan gobarar da ta faru a jihar.

Rahotanni sun bayyana cewa gwamnan ya kwashe tsawon watanni yana tattaunawa da akalla gwamnoni biyu na jam’iyyar ta APC.

Related posts

Leave a Comment