‘Yan Bindiga Sun Yi Awon Gaba Da Mata 20 A Kauyen Katsina

Kimanin Mata ashirin ne aka sace a kauyen Gidan Bido dake karamar hukumar Dandume a jihar Katsina, a lokacin da suka je kauyen domin halartar bikin suna a jiya Juma’a.

Majiyarmu ta tabbatar mata cewa yan bindigar sun zo ne da misalin karfe dayan daren jiya Juma’a dauke da manyan bindigogi, suka sace matan.

Haka zalika, yan bindigar sun kai makamanci irin wannan harin a mahaifar dan Majalisar jihar, mai wakiltar karamar hukumar Dandume a majalisar dokoki ta jihar Katsina, Honarabul Haruna Goma, watau Unguwar Bawa, inda suka sace maza guda biyar duk a daren jiya.

Daga Jamilu Dabawa, Katsina

Related posts

Leave a Comment