‘Yan Bindiga Sun Hallaka Mutane 88 Rana Guda A Jihar Kebbi

Rahotanni daga Jihar Kebbi na bayyana cewar ‘yan bindiga sun tafka mummunan ta’asa na kisan jama’a bayin Allah wadanda ba su jiba kuma basu gani ba, Hukumar yan sanda a jihar Kebbi a ranar Asabar ta tabbatar da kisan mutum 88 da tsagerun yan bindiga suka yi a karamar hukumar Danko/Wasugu na jihar Kebbi.

Kakakin hukumar, Nafi’u Abubakar ya bayyana cewa wannan ya auku ne duk a ranar Alhamis, kamar yadda kamfanin dillancin labarai na ?asa NAN ya ruwaito.

Yace an kashe su ne a hare-haren da aka kai garuruwa takwas a karamar hukumar. A cewarsa, kawo yanzu an gano gawawwakin mutum 88 kuma an tura jami’ai tabbatar da tsaro a yankin.

“An kashesu ne a garuruwan Koro, Kimpi, Gaya, Dimi, Zutu, Rafin Gora da Iaguenge, duka a karamar hukumar Danko/Wasugu na jihar Kebbi,” Abubakar yace. “Da farko, gawawwaki 66 aka gano amma yanzu haka, an gano gawawwaki 88.”

Related posts

Leave a Comment