Ya Kamata Gwamnati Ta Rin?a Saurarar Koken Matasa – Dattawan Arewa

?ungiyar tuntuba ta magabatan Arewa (ACF) a ta yi garga?in cewa ya kamata shugabanni a Najeriya su sani cewa, a wani lokaci ne na saurarar bu?atun jama’a, saboda bai dace ba a cigaba da yin biris da matasa da kuma bu?atunsu ba.

Dattawan Arewa sun bayyana cewa cigaba da yin ko ina kula da bukatun matasa tare da matsalolinsu kan iya janyo gagarumar matsala a kasa, wadda ba’a san iyakar ?arshen ta ba.

Shugaban ?ungiyar Dattawan Arewa na ACF, Audu Ogbeh, ne ya bayyana hakan a wani taron tattaunawa na manyan shugabannin al-umma na ?asa da aka yi a garin Kaduna tarayyar Najeriya.

“Halin da ake ciki na zullumi da fargaba musamman a arewacin ?asar nan babbar barazana ce ga zaman lafiya da cigaban yankin da kuma ?asa baki ?aya,” a cewar Ogbeh.

Kalaman na Ogbeh sun zo ne a kan ga?ar hargitsi da ake fama dashi a wasu jihohi a ?asar nan bayan matasa sun shafe kusan mako biyu suna gudanar da zanga-zanga don ganin sun kawo ?arshen zaluncin ?ansanda.

Dattijo Audu Ogbeh ya ce a halin da ake ciki, akwai bu?atar shugabanni su sauya salo da dabaru, sannan su maida hankali a kan cigaban kasa musamman inda muke fuskantar ?alubale da suka shafi ?angarorin siyasa, tattalin arzi?i da kuma zamantakewa.

“Za mu iya, kuma dole mu fuskanci abin da yake gabanmu ta hanyar zuba hannun jari a harkar ilmi, noma da kiwo da kuma masana’antu. “Dole ne mu tafi da matasa, wadanda dama ?a?anmu ne, sannan mu ha?a hannu da su, mu tallafa musu, har ma mu koya daga gare su.

Lokaci ya wuce da zamu yi watsi dasu da bu?atunsu. Yin biris da matasa tamkar mun da?awa kan mu wu?a ne,” a cewarsa. Shugaban na ACF ya ?ara da cewa; “halin zullumi da fargaba na matasa musamman a arewacin Najeriya babbar barazana ce ga yankin da kuma ?asa baki ?aya.”

“Ina sa ran cewa yanzu, fiye da lokutan baya, shine lokacin da masu ruwa da tsaki za su saka hannu don a magance matsalolin kasa da kuma ceto makomar yaranmu.”

Related posts

Leave a Comment