?ungiyar kafafen ya?a labarai masu zaman kansu ta ?asa, ta bu?aci hukumar kula da Kafafen ya?a labarai ta ?asa NBC da yin duba akan wasu dokoki na hukumar kafin ?akaba tarar Naira miliyan biyar da ya sanya wa ?aya daga cikin ‘ya’yan kungiyar, gidan rediyon Nigerian Info FM, bisa ga zargin gidan rediyon ya ya?a labaran da basu kamata wanda ka iya da rikici.
?ungiyar ta bayyana hakan ne a yayin wani taron gaggawa da ta kira ranar Litinin domin duba wannan lamari a ?ar?ashin jagorancin shugaban kungiyar Mista Guy Murray- Bruce.
“Da akwai wasu sharudda guda uku da muke bukatar hukumar NBC ta cika su kafin sanya wannan tara ta Miliyan Biyar da ta yi.
1- Naira miliyan biyar da hukumar ta sanya a matsayin tara ga ya?a kalaman ?atanci na cikin dokokin hukumar ne wanda ba’a kaddamar da aiki da shi ba, bisa ga haka ya zama wajibi ga hukumar ta duba wannan ?angare ta tabbatar da dokar tukuna, kafin zartar da ita.
2- Lallai ne a fili yake dangane da batun da ake ciki, Hukumar NBC ta zama mai ?ara da zama Alkali a lokaci guda ba tare da bada dama na sauraren sauran ?angare ba.
Dole ne hukumar ta fayyace menene kalaman ?atanci, kuma ya zamana tarar ku?in dukkanin ?angarorin ya?a labarai sun ha?u akai.
3- Kamar yadda muka sani shine aikin Jarida na tafiya ne akan gudanar da bincike da banka?o abubuwa da kuma bada kariya ga ‘yan jaridar gaba ?aya.
Bisa ga haka muna kira ga Hukumar BBC da ta samu zama da mahukunta s ?angaren ya?a labarai wa?anda suka ha?a da ?ungiyar ‘yan jarida ta ?asa NUJ da kungiyar Editoci, da kamfanin dillancin labarai na kasa da sauran su domin duba yadda tsarin dokar tara take ga abin da aka amince cewa kalaman ?atanci ne.