Shugaban Amurka Ya Sha Alwashin Kare Hakkin Musulmi

Shugaban Amurka Joe Biden ya ce zai ci gaba da kare ha??in musulmi a fa?in duniya.

Shugaban ya fa?i haka ne cikin wata sanarwa mai ?unshe da sa?on fatan alheri ga al’ummar musulmi yayin da suka soma azumin watan Ramadan a ranar Talata.

Shugaban ya ce yana alfahari da ya ?age haramta wa wasu ?asashen musulmi shiga Amurka.

“Zan ci gaba da tsayawa kan kare ha??in ?an adam a ko ina, har da ?an ?abilar Uyghur a China da rohingya a Burma da kuma dukkanin musulmi a fa?in duniya.

Ya kuma ce dole a kawo ?arshen barazana da ?yama da ake nuna wa musulmi a Amurka, a cewarsa: “babu wani a Amurka da zai kasance cikin fargaba don bayyana addininsa.”

A nasa ?angaren sakataren harakokin wajen Amurka Antonu J. Blinken bayan ya yi wa musulmi murnar Ramadan ya kuma ce Amurka za ta ci gaba da inganta hul?a da ?asashen musulmi.

Related posts

Leave a Comment