Sharhin Bayan Labarai: Daga Ishaq Idris Gui?i

Jama’a barkanmu da asubahin laraba, ashirin da tara ga watan Zulhijja, shekarar 1441 bayan hijirar cikamakin annabawa kuma fiyayyen halitta, Annabi Muhammad S.A.W. Daidai da goma sha tara ga watan Agusta na shekarar dubu biyu da ashirin.
Da fatan za a yi hakuri, don na yi rubutuna na yau, na kammala shi karfe hudu daidai na asubah, kuma a lokacin na sake shi. Sai dai har zuwa yanzun karfe biyar saura minti ashirin da hudu na asubah ban san inda ya nufa ba ya yi nisan kiwo. Idan ya dawo za a gan shi. In bai dawo ba, sai gobe da asubah na sako wani.
Wannan na daya daga cikin kalubalen da nakan fuskanta. In hana ido bacci in yi rubutu, in sako shi ya yi batar dabo.

Za a iya leka rubutun na ban hakuri na yau a Taskar Guibi da ke DCL Hausa a :

https://www.facebook.com/2356865571252507/posts/2679778662294528/

Is’haq Idris Guibi
Kaduna Nijeriya.

Related posts

Leave a Comment