Sarautar Bamalli: Iyan Zazzau Ya Maka El Rufa’i Kotu

Ɗaya daga cikin wadanda suke nemi saurautar Zazzau, Iyan Zazzau Bashar Aminu ya yi karar gwamnan jihar Kaduna Nasir El-Rufai a kotu kan nada Ahmed Nuhu Bamalli Sarkin Zazzau.

Bashar Aminu na neman kotun ta bada umurnin tsige Nuhu Bamalli sannan ta bada umurnin a nada shi sabon sarkin Zazzau ba tare da wani ɓata lokaci ba.

Acewar karar da Iyan Zazzau din ya shigar, shine ya samu kuri’u mafi rinjaye a zaben da masu zaben sarki suka yi tunda farko don haka shi ya dace ya zama sarkin Zazzau.

A cikin karar da ya shigar a babban kotun jihar Kaduna a ranar Litinin, Aminu na son kotun ta bada umurnin nada shi sarki duba da cewa shine ya fi samun kuri’u mafi yawa a zaben da masu zaben sarki suka yi kamar yadda Daily Nigerian ta ruwaito.

Idan ba a manta ba a ranar 25 ga watan Satumba, masu zaben sarki na masarautar Zazzau karkashin jagorancin Wazirin Zazzau, Ibrahim Aminu suka mika jerin sunayen yarimomi uku don zaben daya daga cikinsu a matsayin sabon sarki.

Wadanda aka mika sunayensu sune Bashar Aminu, Iyan Zazzau da ya samu kuri’u 89; Munir Jafaru, Yariman Zazzau ya samu kuri’u 87; Aminu Shehu Idris, Turakin Karamin Zazzau ya samu kuri’u 53.

Amma a ranar 1 ga watan Oktoban 2020, gwamnan jihar Kaduna ya soke sunayen wadanda masu zaben sarkin suka mika masa. A cewarsa, masu zaben sarkin ba su yi adalci ba ga sauran masu neman sarautar kuma ya bukaci a bawa sauran masu neman sarautar shiga takarar.

Sakataren gwamnantin jihar, Balarabe Lawal ya yi bayanin cewa gwamnati ta bada umurnin yin sabon zabe bayan soke na farko saboda an cire sunayen mutum biyu daga cikin masu neman sarautar.

Daga bisani gwamnan ya nada Ahmed Nuhu Bamalli a matsayin sabon sarki ya yi watsi da zaben na farko da masu zaben Sarkin Zazzau suka yi.

A kofin takardar karar da mai karar ya shigar ya yi karar mutum 10 a kotu da suka hada da Gwamnan jihar Kaduna, Nasir El-Rufai, Attoney Janar na jihar Kaduna; Majalisar Sarakunan Kaduna; Majalisar Masarautar Zazzau; Wazirin Zazzau, Ibrahim Aminu; Fagacin Zazzau, Umaru Muhammad; Makama Karamin Zazzau, Mohammed Abbas; Limamin Juma’an Zazzau, Dalhatu Kasimu Imam; Ambasada Ahmed Nuhu Bamalli.

Labarai Makamanta

Leave a Reply