Kwana guda bayan zazzafar muhawara a majalisar dattawa da ta haddasa dakatar da sanata Abdul Ningi, wanda shi ne shugaban ?ungiyar sanatocin arewacin Najeriya – sanatocin kudancin kasar sun farfa?o da ?ungiyarsu tare da za?ar shugabanni.
?ungiyar sanatocin kudancin ?asar ta za?i sanata, Adetokunbo Abiru mai wakiltar Legas ta gabas a matsayin sabon shugaban ?ungiyar.
A baya dai shugaban masu rinjaye na majalisar dattawan ?asar, Senator Opeyemi Bamidele ne ke jagorantar ?ungiyar.
Sanatoci 51 ne daga jihohin kudancin ?asar 17 suka taro domin farfado da ?ungiyar, wata tara bayan ?addamar da majalisar ta 10.
Sanata Bamidele ya ce ?ungiyar ba sabuwa ba ce domin kuwa tana nan tun lokacin majalisa ta tara, yana mai cewa ayyukan ?ungiyar sun dakata ne sakamakon samun sabon mu?amin shugaban masu rinjaye na majalisar da ya samu.
Hakan na zuwa ne kwana guda da Majalisar Dattijan Najeriya ta dakatar da Sanata Abdul Ningi daga majalisar na tsawon wata uku bayan zargin shi da furta kalaman da ake ganin sun ‘zubar da ?imar majalisar.’