Sanata Kyari Ya Maye Gurbin Abdullahi Adamu A Shugabancin APC


Rahotannin dake shigo mana daga birnin tarayya Abuja na bayyana cewa Shugaban jam’iyyar APC mai mulki Sanata Abdullahi Adamu ya ajiye mukaminsa bayan kwashe shekara daya da ‘yan watanni yana jagorantar jam’iyyar.

Sabon shugaban ri?o na jam’iyyar, Sanata Abubakar Kyari ne ya tabbabar da murabus din Adamu kwana guda bayan kafafen yada labarai a Najeriya suka wallafa labarin cewa rashin jituwa tsakanin Sanata Adamu da shugaba Tinubu ya tursasa masa yar da ?wallon mangwaro

Shugaban jam’iyyar ta APC ya bar mukamin ne kimanin wata biyar bayan ya jagorance ta a zaben shugaban kasar, inda ta yi nasara.

Bayanai sun ce Adamu ya ajiye aikin ne tare da sakataren jam’iyyar na kasa, Sanata Iyiola Omisore.

Akwai dai alamu na cewa an dinga samun takun-saka a cikin jam’iyyar tun bayan da shugaba Tinubu ya kama mulki, kimanin watanni biyu da suka gabata.

Ajiye mu?amin shugaban jam’iyyar zai iya alamta cewa akwai wani babban rikici ne tsakanin ?a?an jam’iyyar da aka kasa samun masllaha.

A lokacin da ya sanar da ajiye mu?amin na Abdullahi Adamu, shugaban ri?on jam’iyyar na ?asa, Abubakar Kyari ya ce Sanata Adamu bai bayyana dalilin ajiye mu?amin nasa ba.

Kwamitin gudanarwa na APC din a zamansa na ranar Litinin ne ya amince da na?a Sanata Abubakar Kyari wanda shi ne mataimakin shugaban jam’iyyar a ?angare arewacin Najeriya a matsayin sabon shugaban ri?o na jam’iyyar.

A watan Maris ?in 2022 ne aka za?i Abdullahi Adamu a matsayin shugaban jam’iyyar APC na ?asa bayan gwamnan jihar Yobe, Mai Mala Buni ya yi shugaban ri?o na kusan shekaru biyu.

Related posts

Leave a Comment