Tsohon mataimakin shugaban ?asa Atiku Abubakar ya yi Allah-wadai da harin ta’addancin da aka kai a ?aramar hukumar Rafi ta jihar Neja. An dai kai harin ne a ?auyen Madaka wanda ya yi sanadiyyar rasuwar Magajin Garin da wasu mutum 20.
Da yake mayar da martani game da harin, Atiku a cikin wani rubutu da ya yi a shafinsa na X (wanda a baya aka fi sani da Twitter) a ranar Juma’a, ya ce Najeriya ta zama “filin mutuwa” a ?ar?ashin Shugaba Bola Tinubu.
Ya yi kira da a gaggauta samar da ?an sandan jihohi. A kalamansa: “Abin takaici ne yadda Najeriya ta zama filin kisa. Kashe mutane da dama da suka ha?a da Magajin Gari, a ranar Alhamis da kuma sace wasu da ba a tantance adadinsu ba da wasu ?an bindiga suka yi a ?auyen Madaka da ke ?aramar hukumar Rafi a jihar Neja, wani tabbaci ne cewa sa?anin tabbacin da ake bayarwa, matsalar rashin tsaro na ci gaba da ta?ar?arewa a ?asar mu.
“Dole ne mu ba da fifiko kan tsaro tare da hanzarta aiwatar da gyaran kundin tsarin mulki wanda zai samar ?an sandan jihohi ta yadda jihohi da ?ananan hukumomi za su iya fito da hanyoyin da suka dace da yankinsu wajen magance wannan matsalar rashin tsaro a ?asar mu. “Ina alhini da addu’a ga iyalan wa?anda suka rasu da kuma gwamnati da al’ummar jihar Neja.”