Yun?urin farko na na?a sabon Sarkin Zazzau ya ci tura inda a yanzu haka masu za?e na Masarautar Zazzau suke sake nazari kan sabon matakin za?en Sarki.
A ranar Laraba da yamma ne gwamnan jihar Kaduna da ke arewacin Najeriya Malam Nasir el-Rufa’i ya wallafa a shafinsa na Tuwita cewa, ”A yanzu haka masu za?en sarki na sake sabon nazari don za?o wa?anda za a za?a cikinsu da zai zama Sarkin Masarautar Fulani ta Zazzau na 19.
”Gwamnatin jihar Kaduna ce ta bayar da umarnin yin sabon zagaye na za?en bayan da ta soke na farko da aka fara, inda aka cire ?an takara biyu.
A sanarwar da gwamnatin jihar ta fitar, ta bayyana cewa soke za?en farkon na da ala?a da cire sunayen wasu ‘yan takara biyu wa?anda suka nuna sha’awar sarautar amma daga baya aka ce musu an rufe karbar sunayen masu son zama sarki.
Gwamnatin jihar ta kuma nuna ?acin ranta dangane da yadda aka tsegunta batun za?en da masu zaben sarki suka yi a ranar 24 ga watan Satumba tun kafin gwamnan jihar ya samu rahoto a hukumance kan za?en.
A ranar Lahadi, 20 ga watan Satumba ne Sarkin Zazzau Dakta Shehu Idris ya rasu bayan fama da gajeruwar rashin lafiya.
Tun bayan rasuwar sarkin, gwamnan jihar ya tsiri karatun litattafai daban-daban inda a halin yanzu ya karanta a?alla litattafai uku kamar yadda ya bayyana.
Ya ce littafan za su taimaka masa wurin yanke hukunci a za?en sarkin ganin cewa shi ne mai wu?a mai nama a ?arshen za?en.