Majalisa Ta Yi Watsi Da Bukatar Tinubu Na Tura Dakarun Soji Nijar

‘Yan Majalisar Dattawan Najeriya sun ?i amincewa da bu?atar neman goyon bayansu da Shugaba Bola Tinubu ya aika kan tura sojojin ?asar zuwa Nijar don tilasta wa sojoji komawa kan tsarin mulki.

Shugaba Tinubu ya nemi goyon bayan ‘yan majalisar ne cikin wata wasi?a da ya aika musu ranar Juma’a, inda ya bayyana musu matakan da ya ?auka a matsayinsa na shugaban ?ungiyar Ecowas ta raya tattalin arzikin Afirka ta Yamma.

Bayan fitowa daga wani zaman sirri a ranar Asabar, Majalisar ta jaddada goyon bayanta ga yun?urin Ecowas, ban da maganar amfani da ?arfin soja.

“Mun ?i amincewa saboda ba abu ne da ya kamata a fara tunaninsa ba ma, saboda abu ne na cikin gida,” kamar yadda Sanata Ali Nudme ya shaida wa BBC.

Sanatan ya ?ara da cewa shawarar da mafi yawan sanatocin suka bayar ita ce a ci gaba da yun?urin sulhu ta hanyar difilomasiyya, maimakon ?arfin soja.

“Muna da shugabannin ?asa, wa?anda sojojin Nijar ke mutuntawa kamar Buhari da Abdulsalam da Babangida da Jonathan, idan aka yi amfani da wa?annan za a samu masalaha,” a cewarsa.

Cikin matakan da Tinubu ya ?auka akwai kulle iyakokin Najeriya da Nijar, da katse wutar lantarkin ?asar.

Related posts

Leave a Comment