Kebbi: Gwamna Ya Amince Da Na?in Sabbin Sarakuna Shidda

Gwamnatin jihar Kebbi karkashin jagorancin Gwamna Atiku Bagudu ta amince da nadin Sarakuna shida, a kananan Hukumomi shida dake fadin jihar.

Nadin ya hada da:-

1) Alhaji Muhammad Aliyu Maiyama, A Matsayin Sarkin Kudun Maiyama.

2) Alhaji Sadiq Ibrahim A Matsayin Sarkin Birnin Kebbi (Ubandoman Birnin Kebbi)

3) Alhaji Tukur Bahindi, A Matsayin Sarkin Bahindi

4)Yakubu Abubakar Kaoje, A Matsayin Sarkin Yamusa

5) Buhari Muhammad Aliero, A Matsayin Sarkin Aliero

6) Hamza Muhammad Na Gwandu, A Matsayin Sarkin Rafin Zuru.

Kwamishinan kananan hukumomi na jihar Kebbi, Hassan Muhammad Shalla ne ya bayyana hakan yau a Birnin Kebbi.

Kwamishinan ya taya Sarakunan murna tare da yi musu fatan alkairi.

Related posts

Leave a Comment