Sanannen malamin addinin musulunci, Sheikh Ahmad Gumi, ya ce sojojin Najeriya suna tsawwalawa a hanyar da suke bi wajen ya?i da ?an bindiga.
Ya ce hanyar da sojojin ke bi domin kawo ?arshen ?an bindigan a yankin Arewacin Najeriya, ta yi tsauri da yawa.
Ya ce dakarun sojoji da na sama sun ?addamar da hare-hare ta ?asa da ta sama da suka hallaka iyalan ?an bindigan, mata da ?a?ansu, lamarin da ya harzu?a su, inda suke ganin hakan a matsayin ya?i.
Malamin ya bayyana hakan ne a wani shiri a shafin X da jaridar Daily Trust ta shirya. Ya dage da cewa bin hanyar amfani da tattaunawa ce kawai za ta dakatar da ayyukan ?an bindiga a yankin Arewa.
Akalamansa: “A gare su (sojoji) suna ya?i ne. Maganar gaskiya sojoji sun tsaurara a kansu, sojojin sama suna kashe iyalansu.” Gumi, wanda a baya ya sha shiga daji domin tattaunawa da ?an bindiga, ya yi kira da abi hanyar da tsohon shugaban ?asa, Umaru Musa Yar’adua ya bi ya magance tsagerun Neja-Delta, domin kawo ?arshen ayyukan ?an bindiga.