Kano: Ganduje Ya Bada Umarnin Komawa Makaranta

Gwamnatin jihar Kano karkashin jagorancin Gwamna Abdullahi Umar Ganduje ta amince da a bude makarantu a jahar Kano inda za a bu?e su daga 11 ga watan Oktoba.

Kwamishinan ilimi na jihar Kano, Sunusi Muhammad Kiru ne ya sanar da hakan a yau.

Ya bayyana cewa ‘yan aji shida da biyar na firamare za su koma makaranata a ranar 11 ga watan Oktoban 2020.

‘Yan aji ?aya da biyu kuma za su rin?a zuwa makaranta a ranakun Litinin da Talata kawai, inda za su fara daga 12 ga watan Oktoba.
Sai kuma ‘yan aji uku da hu?u da biyar na makarantun firamare su ma za su rin?a zuwa Laraba da Alhamis da Juma’a inda za su koma 12 ga watan Oktoba

Related posts

Leave a Comment