Kaduna: ‘Yan Bindiga Sun Yi Garkuwa Da Shugaban Kungiyar ‘Yan Jarida Da Iyalansa

IMG 20240707 152749

Rahotannin dake shigo mana daga Jihar Kaduna na bayyana cewa ‘yan ta’adda masu Garkuwa da mutane  sunkai hari jiya asabar a unguwar  Danhoni, dake cikin Karamar hukumar Chikun Jihar Kaduna Sunyi awon gaba da yan jaridu 2 da iyalansu.

‘yan jaridar sune Abdulgafar Alabelewe Na jaridar ( The Nation)  da Abduraheem Aaodu na  jaridar The Nation da (Blueprint) anyi Garkuwa da su a Daren Asabar a cikin gidajensu.

Alabelewe shine shugaban kungiyar wakilan kafafen yada labarai na kasa reshen Jihar Kaduna, an sace shi ne tare   da matarsa da yaransa Guda  Biyu, yayin da Abdulrahim Aaodu Wanda shime an sace  shi tare  matarsa aka bar yarinyarsa wadda akace bata da lafiya.

Daya daga cikin iyalan wadanda  aka sacen Taofeeq Olayemi ya shaida wa manema labarai cewa maharan sun shigo unguwar  da misalin karfe na  Goma da rabi na dare (10:30pm) suka rinka harbin mai uwa da  wabi daga bisani suka  balla kofofi da tagogi gidan

Olayemi yace tunda farko yan ta’addan sun tsallaka gidan  Abdulgafar  inda suka wuce kaitsaye dakinsa sukai awon gaba dashi da matarsa da yayansa guda uku da bakuwa guda daya Wanda daga bisani suka sako bakuwar da yarinya daya cikin ‘ya’yansa sannan suka balle kofar Dakin Aaodu suka dauke shi da matarsa sukabar yarinyarsa wadda bata da lafiya.

Kokafin jami’an ‘ yan sakai  su zo maharan sun gudu kuma har izuwa hada wannan rahoton ba kiran waya daga yan’taddan.

Related posts

Leave a Comment