Kaduna: Muna Kokarin Dawo Da Shugabannin Kananan Hukumomin Da Aka Dakatar – Hon Jaja

Shugaban kungiyar shugabannin kananan Hukumomin Jihar Kaduna Honorabul Shu’aibu Bawa Jaja yace kungiyar tasu na iyaka bakin kokarinta wajen ganin an daidaita ?angaren majalisa da wasu shugabannin kananan hukumomi 3 da majalisar ta dakatar.

Bawa Jaja ya sanar da hakan ne a yayin wata tattaunawa da manema labarai da ya yi a ofishin sa dake ma’aikatar kula da ?ananan hukumomi dake Kaduna.

Shugaban kungiyar ya ?ara da cewar dukkanin shirye shirye da matakan da ya kamata a ?auka sun yi nisa wajen shawo kan matsalar wanda ya bayyana shi a matsayin na rashin fahimta.

Daga karshe Bawa Jaja ya bada tabbaci ga jama’ar Kaduna cewa a matsayin su na shugabannin kananan hukumomi za su yi dukkanin mai yiwuwa wajen ciyar da jihar Kaduna gaba.

Related posts

Leave a Comment