Jonathan Ya ?ora Najeriya A Turba Ta ?warai – Buhari

Shugaban ?asa Muhammadu Buhari ya taya tsohon shugaban ?asa Goodluck Jonathan murnar cika shekara 63 da haihuwa.

A cikin wata sanarwa da mai taimaka masa ta fuskar ya?a labarai Femi Adesina ya fitar ranar Alhamis, Buhari ya ce Jonathan ya janyo wa Nijeriya martaba da ?ima a idon duniya.

Buhari ya ce jajircewa da dattakun tsohon shugaban ?asar a siyasar Nijeriya ce bar ta kai shi ga jagorantar tawagar ?ungiyar ECOWAS ta samar da zaman lafiya a ?asar Mali.

Tsohon shugaba Jonathan dai ya kafa tarihi a yankin nahiyar Afirka kasancewar shi Shugaba na farko da ke kan Karagar mulki da ya amince da shan kaye a hannun abokin hamayyar shi.

A zaben 2015 Jonathan ya amince da shan kaye a hannun Shugaba Buhari, inda ya bayyana cewar ya yi hakan ne domin kariya daga tsare dukiyoyi da rayukan ‘yan Najeriya, wanda ?in amincewar shi na iya haifar da matsala.

Related posts

Leave a Comment