Mataimakin Shugaban Najeriya Farfesa Yemi Osinbajo ya bai wa ‘yan ?asar ha?uri game da “jan ?afar da gwamnati ta yi” kan gyaran ayyukan rundunar ‘yan sandan ?asar.
Cikin wata sanarwa da ya wallafa a shafinsa na Twitter, ya ce yana sane da cewa matasa na cikin fushi game da abin da rundunar SARS take aikatawa “kuma suna da dalilin yin hakan”.
Kusan mako biyu kenan aka shafe ana zanga-zanga a wasu jihohin Najeriya ta yin Allah-wadai tare da kiran da a kawo ?arshen ayyukan rundunar SARS ta ‘yan sanda, wadda ke ya?i da fashi da makami sakamakon zargin cin zarafin ‘yan ?asa da kashe mutane ba tare da shari’a ba.
Tun a ranar Lahadi, 11 ga watan Oktoba ne Sufeto Janar na ‘Yan Sanda Muhammed Adamu ya sanar da rushe SARS, sai dai har yanzu ba a daina zanga-zanga ba.
“Ya ku ‘yan Najeriya, na sani cewa da yawa daga cikinku ransu a ?ace yake, cewa ya kamata mu ?auki matakai cikin sauri. Saboda haka muna neman afuwarku,” in ji Osinbajo.
a Najeriya sanye da hijabi?
A ranar Alhamis ne Osinbajo ya jagoranci zaman Majalisar Tattalin Arziki ta Najeriya – wadda ta ha?ar da gwamnonin jihohi 36 har da ministan Abuja – inda suka zayyana wasu matakai da za su ?auka kamar yadda masu zanga-zanga suka bu?ata.
Osinbajo ya ce: “Na sani sarai yadda matasa ke ji. Da yawa na jin cewa mun yi gum da bakinmu kuma ba mu yi komai ba. Kuna da dalilin yin hakan.
“Tun daga makon da ya gabata, muna bin zanga-zangar kuma na yi tattaunawa da masu ruwa da tsaki da ya kamata ku sani. Gaskiya na ?aya daga cikin rukunan gudanar da mulki.”
Daga cikin sakamakon zaman Majalisar Tattalin Arziki ta ?asa da Osinbajo ya jagoranta, akwai kafa kwamitocin bincike a kowacce jiha da zai za?ulo wa?anda ‘yan sanda suka ci zarafi “domin yi musu adalci”.
Mataimakin shugaban ?asar ya ce “na san burinku shi ne ku gani a ?asa kuma ina fa?a muku cewa ana tsaka da yin aiki”.
Wajibi ne kowacce jiha ta kafa kwamitin shari’a domin binciken cin zarafi da ‘yan sanda suka aikata wanda zai kasance ?ar?ashin shugabancin:
Tsohon al?alin kotun tarayya
Wakilai biyu daga ?ungiyoyin farar hula
?an sanda ?aya mai ritaya
Wakilin matasa guda ?aya
Wakilin ?alibai guda ?aya
Wakilin antoni janar na jihar guda ?aya
Wakili guda ?aya daga Hukumar Kare Ha??i ta ?asa
Aikin kwamitin
Kar?a tare da bincika ?orafin cin zarafi ko kisa da ‘yan sanda suka aikata
Tantance shaidu da aka gabatar tare da tabbatar da gaskiyarsu
Bayar da shawarar biyansu diyya da kuma matakin gyara da za a iya ?auka
Kwamitin zai gudanar da aikinsa ne cikin wata shida – sai dai idan gwamna na da wani ?wa??waran dalili na tsawaita shi
Kazalika, majalisar ta umarci kowanne gwamna da ya kafa wata gidauniya mai suna Victims Fund da za ta biya wa?anda aka ci zarafi diyya.
Mataimakin shugaban na Najeriya ya ce babu wani ?an sanda da ya yi aiki a SARS da za a sanya a cikin sabuwar rundunar SWAT.
BBC HAUSA