A yau Alhamis gwamnatin tarayya ta amince a bude makarantu. Inda tuni jijohin Lagos, Ondo, Kogi da sauransu suka soma shirin bude makarantu a cikin wannan wata.
Haka kuma gwmnatin ta amince a bude sansanonin horas da yi wa ?asa hidima (NYSC). Ta kuma sassauta dokar hana zirga zirga zuwa karfe 12am – 4am. Tare da amincewa a dawo da zirga zirga ta sufurin jiragen sama.
?aliban makarantu a Najeriya dai sun lashe kimanin watanni shida suna zaune a gida, tun bayan sanar da ?ullar cutar sar?ewar numfashi ta CORONA.
Ana sa ran hukumomin makarantun za su bi dokoki da ?a’idoci na Hukumar da?ile ya?uwar cututtuka ta ?asa wato NCDC ta hanyar ba da tazara sanya takunkumi da wanke hannu.