Fitinar ‘Yan Bindiga: Buhari Ya Gana Da Gwamnonin Arewa

Shugaban kasa Muhammadu Buhari ya sake tabbatar wa Gwamnonin Arewa cewa gwamnatin sa za ta kawo karshen matsalar tsaro a Arewa, matsalar kuwa ko ma wace iri ce.

Gwamnonin Arewa sun kai wa Shugaba Buhari wannan ziyara ce bisa jagorancin Shugaban Kungiyar Gwamnaonin Arewa, Simon Lalong na Jihar Filato.

A wannan ganawar da ya yi da su ne a ranar Alhamis, Shugaba Buhari ya sake sha masu alwashin kawo karshen dukkan matsalolin tsaro a Arewa baki daya.

Sun yi wannan ganawar ce a ranar da aka yi jana’izar mutum kusan 80 da ‘yan bindiga su ka kashe a garin Magami, cikin Jihar Zamfara.

Wadanda su ka halarci ganawar sun gada da Shugaban Kungiyar Gwamnonin Arewa, Simon Lalong na Jihar Filato, Governor Simon Lalong, Gwamnan Kebbi, Atiku Bagudu; Kaduna, Nasir El-Rufai; Yobe, Mai Mala-Buni, Niger, Abubakar Bello; da Nasarawa, Abdullahi Sule.

A wurin ganawar akwai Shugaban Ma’aikatan Fadar Shugaban Kasa, Ibrahim Gambari.

A taron dai gwamnonin sun rika yin magana daya bayan daya dangane da kokarin da kowanen su key i wajen ganin an samar da tsaro a jihar sa, tare kuma da neman abin da ya ke bukata gwamnatin tarayya za ta yi a kan lamarin.

Da ya ke magana da manema labarai bayan tashi daga taron a Fadar Shugaban Kasa, Lalong bayyana masu cewa Shugaba Buhari na da yakinin ganin ya kawo karshen matsalar tsaro a kasar nan.

Ta kara jaddada masu cewa babu wani batu da su ka tattauna da Shugaba Buhari baya ga na matsalar da ta fi damun Arewa, wato matsalar tsaro.

Related posts

Leave a Comment