Da Dumi-Dumi: Kungiyar ASUU Ta Janye Yajin Aiki

Daga Comr Abba Sani Pantami

Kungiyar malaman Jami’o’i ta dakatar da yajin aikin da ta kwashe watanni takwas tana yi, duk da cewa kungiyar ba ta fitar da sanarwar a hukumance ba, amma wakilin jaridar Punch ya tattaro cewa an dauki matakin ne a karshen taron majalisar zartarwa ta kasa da aka gudanar a sakatariyar ASUU da ke Abuja.

Da yake zantawa da wakilin jaridar Punch wata majiya mai cikakken bayani a cikin hukumar ta NEC ta ce, “Eh, an dakatar da shi”.

Da aka nemi karin bayani, majiyar ta ce, “Shugaban zai fitar da wata sanarwa a hukumance da wannan safiyar ta jumma’a”.

Related posts

Leave a Comment