Cin Hanci Da Rashawa: Hukumar Shige Da Fice Ta Kori Jami’ai 60

Hukumar Kula da Shiga da Fice ta ?asa ta ce ta kori jami’anta 60 bayan an kama su suna kar?a ko bada toshiyar baki.

Shugaban hukumar, Muhammad Babandede ne ya sanar da hakan a hirar sa da BBC Hausa a ranar Asabar 10 ga watan Oktoba.

Ya kuma ce ya ta?a yin ?adda-kama a matsayin mai shara domin ya cafke masu kar?ar toshiyar baki.

Babandede ya ce an kori jami’an 60 ne cikin shekaru hudu da suka shude bayan anyi ?arar su “tare da hujjoji” da aka gabatar wa hukumar ta hannun Ma’aikatan Harkokin Cikin Gida.

“Kimanin shekaru hudu kenan da muka hana bada toshiyar baki don tura jami’ai wuraren ayyuka masu kyau kamar yadda aka saba a baya.

?ar?ashin Ma’aikatar Cikin Gida, Mun sallami jami’ai 60 da aka kama da laifin rashawa a filayen jiragen sama da toshoshin ruwa,” in ji shi.

“Akwai gur?atattun jami’ai har cikin manya. Amma hakkin mu ne a matsayin shugabanni mu hana hakan musamman batun bada cin hanci don tura jami’ai boda da tashoshin jiragen ruwa.

Mun kuma hana jam’i a da ke aiki a wuraren kai wa manyan su kudi. Duk wanda aka kama zai gane kurensa.

Na ta?a yin shiga irin ta masu shara a filin tashin jiragen sama da tashan jirgin ruwa don in kama gur?atattun jami’ai. Ba zamu iya aikin mu kadai ba musamman yanzu da sauran hukumomin tsaro ke taya mu tsare iyakokin ?asa,” in ji Babandede.

Har wa yau, ya ce dole duk wata hujja da za a gabatar game da jam’in da ake zargi da kar?a ko bada rashawa ya zama sahihi.

Related posts

Leave a Comment