An na?a Mahamat Idriss Deby Itno a matsayin shugaban gwamnatin ri?o a kasar Chadi.
Matakin ya biyo bayan mutuwar mahaifinsa, Idriss Deby a yau Talata sakamakon raunukan da ya ji a kusa da kan iyakar Chadi da Libya inda ‘yan tawaye ke bore.
Shugaban na riko na da shekaru 37 a duniya kuma Mahamat Idriss Deby Itno babban janar na soja ne mai anini uku a rundunar sojin Chadi.
A wata sanarwa da ya gabatar a gidan talabijin, mai magana da yawun rundunar sojin ?asar Janar Azem Bermandoa Agouna ya ce, Shugaba Idriss Déby na Chadi “ya ja numfashinsa na ?arshe a yayin da yake kare martabar ?asar a fagen daga”.
Majalisar ?oli ta soji za ta jagoranci ?asar har na tsawon wata 18 karkashin jagorancin Mahamat Idriss Deby
Mista Déby ya ?are mulkin ?asar ne tun a shekarar 1990.
A ?arshen mako ne ya je fagen daga don kai wa dakarun da ke ya?i da ?an tawaye ziyara a kusa da kan iyakar Libiya.
Deby ya rasu ne yayin da yake kan hanyar lashe za?e wa’adi na shida sakamakon za?en da aka gudanar ranar 11 ga watan Afrilu.