Rahotanni daga Maiduguri babban birnin Jihar Borno na bayyana cewar Rundunar Sojin Najeriya ta samu nasarar damke kasurgumin dan Boko Haram a Arewa maso gabas kuma ta kai simame ma’ajiyar sinadaran hada bama-bamai a Borno da Yobe.
Daraktan hulda da jama’a na hukumar, Birgediya Janar Onyema Nwachukwu, ya bayyana hakan a jawabin da ya fitar a shafin Facebook na hukumar.
Yace wannan nasara ya biyo bayan hare-haren da rundunar Operation HADIN KAI (OPHK) suka kai. Yace: “Dakarun Sector 2 Joint Task Force na Operation HADIN KAI (OPHK) sun damke wani babban dan Boko Haram kuma sun kai simame ma’ajiyar ajiyan sinadaran hada bama-bamai a Damboa dake jihar Borno; da kuma Gashua dake jihar Yobe.”
“Sakamakon cinne, an damke wani dan ta’addan BH/ISWAP da aka dade ana nema ruwa a jallo a hanyar Damboa-Wajiroko.” Inji sanarwar.
Ya kara da cewa Sojoji sun kwato buhuhunan sinadarin Urea 281 a ma’ajiyoyi daban-daban kuma an damke masu kaiwa Boko Haram wadannan kayayyaki mutum biyu.
“Hakazalika, Sojoji sun samu nasarar damke wasu masu kaiwa yan ta’adda sinadaran hada bama-bamai. Kasuwar ta shahara da taya yan Boko Haram boye sinadaren.” “A harin da aka kai, an damke buhuhunan Urea 281 daga kasuwar kuma an damke masu sayarwa Boko Haram.