Labarin dake shigo mana daga Jihar Kano na bayyana cewa wata babbar kotu a jihar ta yanke hukuncin cewa hukumar kar?ar ?orafe-?orafe da ya?i da rashawa ta jihar ba ta da ikon ta gayyaci ko ma ta gudanar da bincike kan tsohon gwamnan Kano kuma shugaban Jam’iyyar APC ta ?asa, Abdullahi Umar Ganduje game da bidiyon dala.
Mai shari’a Abdullahi Muhammad Liman ne ya yanke hukuncin ranar Talata a ?arar da Ganduje ya shigar kan hukumar ta PCACC, kamar yadda jaridar Daily Trust ta ruwaito.
Ganduje ya shigar da ?arar a watan Yulin 2023 inda ya nemi a kare masa ?ancinsa bayan da shugaban hukumar Muhyi Magaji Rimin Gado ya gayyace shi da ya bayyana domin amsa tambayoyi kan bidiyon dala.
Kotun ta ba da umarnin hana gayyata ko kuma bincikar Ganduje har sai abin da kotu ta tsayar a ?arshe.
A 2018 ne jaridar Daily Nigerian ta wallafa wani bidiyo da ya kara?e shafukan sada zumunta a lokacin da Ganduje yake gwamna, bidiyon ya nuna shi yana kar?ar damun daloli daga hannun wani ?an kwangila.
Sai dai Ganduje ya musanta zargin inda ya ce ha?a bidiyon aka yi.
Lauyan hukumar ta kar?ar ?orafe-?orafe, Usman Fari ya ce ya ?auki lokaci mai tsawo kafin kotun ta yanke hukunci a ?arar da aka shigar tun Yulin bara inda ya ce tuni ya samu izinin wanda yake ?arewa domin ?aukaka ?ara.
Lauyan Ganduje, Mathew Burkaa mai mukamin SAN ya ce hukuncin kotun ya tabbatar da matsayinsa cewa hukumar ba za ta iya yin bincike kan wanda yake karewa ba kan wata doka da ke ta tarayya.