Bauchi: Gwamna Bala Ya Tube Rawanin Masu Sarauta Shidda

Rahotannin dake shigo mana daga Jihar Bauchi na bayyana cewa Gwamnatin jihar ta tabbatar da korar hakimai da dagatai shida saboda a cewarta an same su da shiga harkokin siyasa da cin iyakar gandun dazuka ba bisa ?a’ida ba.

Matakin korar wanda ya shafi masu ri?e da sarauta a masarautun Bauchi da Katagum, yana ?unshe ne a sanarwar da Babban Sakataren ri?o a hukumar kula da harkokin ?ananan hukumomi, Nasiru Ibrahim ya fitar.

Mutanen da lamarin ya shafa a cewar sanarwar, sun ha?ar da Hakimin Udubo, Alhaji Aminu Muhammad Malami da Hakimin Azare Alhaji Bashir Kabir Umar da Dagacin Gadiya, Umar Omar da Dagacin Tarmasawa, Umar Bani dukkansu a masarautar Katagum.

Sai kuma Dagacin Beni Bello Suleman da Dagacin Badara, Alhaji Yusuf Aliyu Badara a masarautar Bauchi.

Sanarwar ta ambato hukumar na cewa ta amince da korar masu ri?e da sarautun ne saboda shiga harkokin siyasar jam’iyya da aikata ba daidai ba da cin iyakar dazuka ba bisa ?a’ida ba da sare itatuwa da ?arnatar da dukiyar jama’a da rashin biyayya, wa?anda suka sa?a da dokokin aikin gwamnati.

Related posts

Leave a Comment