Ahmed Musa Ya Bada Gudummuwar Miliyan Biyu Domin Gina Masallaci

Rahotanni daga birnin Kano na bayyana cewar ?an Kwallon Nijeriya, Ahmed Musa Ya Bada Tallafin Naira Milyan Biyu Domin Gina wani katafaren Masallaci a birnin Kano.

Za a gina masallacin ne a makarantar sakandire ta sojoji dake Barikin Bukavo a jihar Kano.

A kwanakin baya ne dai Ahmed Musa ya shelanta cewa ya dawo buga wasan ?wallon kafa a ?ungiyar kwallon kafa ta Kano Pillars dake Kano.

Masana dai sun bayyana Ahmed Musa a matsayin ?aya daga cikin attajiran ‘yan wasan ?wallon ?afa a duniya wanda tauraron su ke haskawa.

Related posts

Leave a Comment