?atanci Ga Annabi: Shehu Sani Ya Yi Tir Da Faransa

Tsohon ?an Majalisar Dattawa mai wakiltar maza?ar Kaduna ta tsakiya majalisar Dattawa Kwamared Shehu Sani, ya ce dole ayi tir da masu ta’addanci da rigar musulunci a kasar Faransa, sai dai wannan bai hana shi yin tir da aikin Shugaba Macron ba.

?an siyasar ya ce babu abin da zai hana a fito a yi tir da abin da shugaban kasar Faransar ya yi na ba masu yi wa addinin musulunci isgilanci goyon-baya.

“Ya kai @EmmanuelMacron, dole ayi tir da duk wani harin ta’addanci ko zagon-kasa da aka yi a kasar Faransa da sunan musulunci, tsantsar hauka ce da tsantsangwaron rashin imani.”

“Mara baya kai-tsaye ko a kaikaice da ka ke yi ga masu bata musulunci ko cin mutuncin Annabi Muhammad (tsira da aminci a gareshi), duk shi ma abin ayi Allah-wadai ne.”

Sani wanda ya wakilci Kaduna ta tsakiya majalisar dattawa tsakanin 2015 zuwa 2019, ya yi wannan magana ne a shafinsa na Twitter a ranar Litinin.

Related posts

Leave a Comment