?ungiyar Kasuwanci Ta Duniya: Ngozi Ta Nemi Gudummuwar Buhari

Shugaban kasa, Muhammad Buhari, ya tabbatarwa da Ngozi Okonjo-Iweala, tsohuwar ministar ku?i, cewa gwamnatin tarayya zata yi duk mai yiwuwa don ganin ta zama shugabar ?ungiyar kasuwanci ta duniya(WTO).

Buhari ya yi al?awarin ne yayin da Okonjo-Iweala ta kai masa ziyara a fadar shugaban ?asa da ke birnin tarayya, Abuja.

Okonjo-Iweala da Yoo Myung-hee (ministar kasuwanci ta ?asar koriya ta kudu), sune ?an takara da suka kai matakin ?arshe na neman kujerar ?ungiyar kasuwanci ta duniya (WTO).

Duk wadda ta samu nasarar lashe zaben kujerar a tsakaninsu itace za ta kasance mace ta farko da ta ta?a shugabantar ?ungiyar kasuwanci ta duniya tun daga kafa ?ungiyar shekaru ashirin da biyar da suka gabata.

A cewar Buhari,Okonjo-Iweala ita tafi cancanta da samun matsayin idan aka yi duba ga irin ?wazo da kuma himma da ta ke da shi a gudanar da aikinta a ?asa dama duniya baki ?aya.
“Ina mai tabbatar da cewa za muyi duk yadda zamu iya don ganin kin zama shugabar ?ungiyar kasuwanci ta duniya (WTO). “Ba wai kawai don ke ?ar Najeriya ba ce, saboda ke ?ar ?asa ce mai ?wazo da kuma aiki tu?uru.

Kin cancanci hakan.”Acewar Buhari. Buhari ya da?a tabbatar mata da cewa zai tuntu?i wasu shugabannin duniya ta hanyar kiran waya da kuma wasi?a don neman goyon bayansu.

“Na yi irin hakan ga Dr Akinwunmi Adesina da ya nemi Shugaban Bankin cigaban Afirka (AfDB). Dukkaninku kun yiwa kasa aiki a ?ar?ashin jam’yyar PDP. Gaba?ayanku kun cancanta matu?a,” a cewarsa.

Yayin da ta ke magana a kan goyon bayan shugaban ?asar, Ngozi ta ce tana alfahirin zama ?ar Najeriya. Ta kuma jinjinawa shugabannin ?ungiyar tattalin arzi?in ?asashen yammacin Afirka a bisa nuna kulawarsu.

Ta ro?i Buhari da ya yi yun?uri na ?arshe cikin satin nan don ganin Koriya ta sha kaye sannan Najeriya ta samu nasara ta hanyar tuntu?ar manyan shugabannin duniya.

Ta kuma godewa sauran wa?anda suka nuna goyon baya gareta. “Ina matukar alfaharin kasancewa ?ar Najeriya. Na samu goyon baya sosai daga mai girma shugaban ?asa, shugaban ma,aikata, ministan harkokin ?asashen waje, ministan masana’antu, kasuwanci da zuba hannun jari.

“Ministocin sun yi aiki tu?uru don ganin na samu nasara,” a cewar Okonjo-Iweala. “Shugaban ?asa ya sakani farin ciki, ina alfahari da ?asata,” a cewarta.

Related posts

Leave a Comment